Mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka Kurt Campbell ya fada a ranar Litinin cewa gwamnatin Biden ba ta ganin akwai yuwuwar Isra’ila ta samu “cikakkiyar nasara” wajen fatattakar Hamas a yankin Gaza na Falasdinu.
Firaiminista Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Alhamis cewa barazanar da Amurka ta yi na hana makamai ba za ta hana Isra’ila ci gaba da kai hare-hare Gaza ba, lamarin da ke nuni da cewa za ta iya yin gaban kanta wajen mamaye birnin Rafah mai cunkoson jama’a ba tare da goyon bayan babbar kawarta ba
Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce da sanyin safiyar Juma’a Yarima Harry zai gana da Babban Hafsan Hafsoshin rundunar tsaron Najeriya, Janaral Christopher Gwabin Musa.
Shugaba Joe Biden ya fada jiya Laraba cewa ba zai aika da muggan makamai ga Isra'ila da za ta iya amfani da su wajen kai hare-haren wuce gona da iri kan Rafah ba, wanda yake tungar karshe ta Hamas a Gaza, saboda nuna damuwa kan yadda zai afka kan fararen hula fiye da miliyan 1 da ke fakewa a wurin.
Duk da cijewar da tattaunawar Isira'ila da Hamas ta yi, Amurka na fatan bangarorin biyu za su cimma jituwa kan sauran bambancin da ke tsakaninsu don a samu tsagaita wuta.
Putin ya sake samun sabon wa’adin mulki na shekaru 6 a watan Maris din daya gabata bayan daya lashe zaben shugaban kasar da aka yi ba tare da wata hamayya ba.
Kungiyar mayaka ta Falasdinu a jiya Litinin ta amince da shawarar tsagaita bude wuta a Gaza daga masu shiga tsakani, sai dai Isra'ila ta ce sharuddan ba su biya bukatunta ba, kuma za ta ci gaba da kai hare-hare a Rafah yayin da take shirin ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar.
Isra'ila ta ba da umarnin rufe ofisoshin gidan talabijin na Aljazeera na Qatar da ke kasar a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da ya kara dagula takaddamar da ke tsakanin tashar watsa labaran da gwamnatin Firaminista Benjamin Netanyahu.
Wani jami'in Amurka ya fada a ranar Alhamis cewa Rasha ta tura wasu sojojinta zuwa wani sansanin sojin sama a Jamhuriyar Nijar inda wasu 'yan tsirarun sojojin Amurka suka rage bayan da akasarin sojojin Amurka suka fice daga sansanin da ke Yamai babban birnin kasar.
Daruruwan ‘yan sanda masu hular kwano ne suka kutsa da karfin tuwo zuwa tsakiyar wani filin taro a Jami’ar California a birnin Los Angeles da safiyar yau Alhamis domin wargaza sansanin da masu zanga zangar goyon bayan Falasdinawa suka kafa da magoya bayan Isra’ila suka kai musu hari cikin dare.
Nan bada dadewa ba tawagar Kungiyar Hamas ta Falasdinawa zata isa kasar Misra domin shiga tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza, a cewar wata sanarwar da kungiyar ta fitar yau Alhamis.
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya bayyana a ranar Laraba cewa, Turkiyya za ta bi sahun Afirka ta Kudu wajen shigar da kara kan kisan kiyashin da Isra'ila ke yi a kotun kasa da kasa (ICJ).
Domin Kari
No media source currently available
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Kungiyoyin tabbatar da ka’ida a hada-hadar tattalin arziki a Malawi sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta magance wasu matsaloli da ke tattare da tsarin bayar da kwangiloli na kasar.Wani rahoto a 2021 ya nuna cewa harkokin bayar da kwangiloli na gwamnati a kasar suna dabaibaye da cin hanci da rashawa
Hukumomi a Najeriya sun daura damarar yaki da magudin zabe, a wani muhimmin lamari ga dimukradiyya a Afirka. Bayan babban zaben 2023, Najeriya ta fara daukan matakan hukunta wadanda aka samu da laifin magudin zabe domin dawo da martabar tsarin zabe a kasar.
A farkon wannan shekarar, kungiyar dake fafutukar yaki da cin hanci ta kasa da kasa, Transparency International, cikin rahotonta na 2023, ta ce yaki da matsalar cin hanci da rashawa a Afirka ya fuskanci koma-baya sosai, inda a wasu kasashen, babu wani abu da aka cimma a game da haka.
Hukumomi a Najeriya su na duba yiwuwar bullo da jami’an ‘yan sanda mallakin jihohi a fadin kasar a wani bangare na magance hare-haren ‘yan bindiga, da garkuwa da mutane da kuma ‘yan fashin daji. ‘Yan Najeriya dai sun yi maraba da wannan yunkuri, sai dai suna cike da shakku.